Isa ga babban shafi

Akwai sauran wadanda suka tsira daga kisan kare dangin yahudawa sama da dubu 254 a duniya-Bincike

Wani rahoton bincike ya nuna cewa akwai sauran mutane da suka tsira daga kisan kare dangi da Hitla na Jamus ya yiwa yahudawa da yawan su ya kai 245 a doron kasa.

Prime ministan Isra'il Benjamin Natenyahu
Prime ministan Isra'il Benjamin Natenyahu via REUTERS - POOL
Talla

Kungiyar Claims Conference mai tattara irin barnar da wannan yaki ya haifar da kuma nemawa wadanda abin ya shafa hakkokin su ta ce cikin wannan adadi guda 119,300 na zaune a cikin Isra’ila yayin da guda 38,400 ke rayuwa a Amurka sai kuma guda 21,900 a Faransa da kuma guda 14,200 da ke zaune yanzu haka a Jamus.

Bayanai sun ce kusan dukannin wadannan mutane, na kananan yara lokacin da wannan rikici ya faru, kuma sun rayu ne a tsakanin sansanonin gudun Hijira da kuma hijira daga kasa zuwa kasa lokacin da suke yunkurin buya da kuma boye asalin su.

Tun bayan samar da kungiyar a shekarar 1951 ta yi nasarar karbar diyya daga Jamus da yawan ta ya kai dala biliyan 90, bayan yarjejeniyoyi daban-daban da aka rika kullawa.

Kungiyar ta ce cikin mutanen akwai wadanda ke fama da tabin kwakwalwa da sauran cututtuka da suka shafi bangarorin jiki wadanda suka samu a sakamakon tashin hankalin da suka gamu da shi lokacin yakin.

Wannan a iya cewa shine kammalallen rahoto na adadin mutanen da suka tsira daga wancan tashin hankali kuma suke a raye har yanzu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.