Faransa ta sha alwashin kawo karshen hare-haren da ake kai wa matasa
Gwamnatin Faransa na duba yuwuwar yadda za a kawo karshen hare-haren da ke faruwa a tsakanin matasa, bayan cakawa wani dan shekara 15 wuka da wani matashi ya yi a karshen mako, daya daga cikin jerin hare-haren da ya girgiza al’ummar kasar.
Wallafawa ranar:
Firaministan Faransa Gabriel Attal ya shirya tarurrukan da jam'iyyun siyasa kan yadda za a tunkari wannan matsala da ke neman wuce gona da iri.
Kasar Faransa dai ta fuskanci jerin hare-hare kan matasa daga takwarorinsu a 'yan makonnin nan, inda masu tsatsauran ra'ayi da masu ra'ayin mazan jiya suka danganta wannan matsala da manufofin gwamnati na sassauta sha’anin shige da fice.
A harin baya-bayan nan, an kashe wani matashi dan shekara 15 a wani artabu da aka yi a garin Chateauroux da ke tsakiyar kasar Faransa ranar Asabar.
Ko da yake an tsare matashin tare da mahaifiyarsa mai shekaru 37, inda za a gurfanar da su gaban kotu nan da ‘yan kwanaki.
Masu gabatar da kara na zargin mahaifiyar matashin da ya aikata danyen aiki da hannu a ciki.
A farkon wannan watan, firaminista Attal, ya ba da sanarwar daukar wasu matakai na murkushe tashe-tashen hankulan matasa a makarantu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu