Isa ga babban shafi

Wakilai 160 ne za su halarci taron zaman lafiya kan Ukraine a Switzerland

Ma’aikatar harkokin wajen Switzerland ta ce ƙasar ta gayyaci sama da wakilai 160 zuwa taron laluɓo zaman lafiya a Ukraine, sai dai Rasha ba ta cikin su.

Wasu mahalarta taron zaman lafiya kan Ukraine a Hague.
Wasu mahalarta taron zaman lafiya kan Ukraine a Hague. © Piroschka Van De Wouw / Reuters
Talla

Rasha, wadda ta ƙaddamar da mamaya a  kan Ukraine a watan Fabarairun shekarar 2022 ta yi watsi da taron, inda ta ke cewa Amurka ce ta shirya shi.

Ta sha nanata cewa ba za ta shiga wata tattaunawa a geme da wannan batu ba har sai Ukraine ta amince da ƙarbe aƙalla kashi 20 na ƙasarta da ta mamaye a halin yanzu.

Ya zuwa yanzu, babu wata masaniya a game da ko shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky  da na Amurka Joe Biden za su samu halartar taron.

Wani lamarin da ake shakku a kai shine ko babbar aminiyar Rasha, wato China za ta samu halartar taron.

Ko da sau ɗaya, China ba ta taɓa caccakar Rasha a game da mamayar Ukraine da ta yi ba, kana ana zargin ta da mara wa Rasha baya  a kan yaƙin.

Taron, wanda zai gudana a ƙarshen mako zai kasance ne daga ranar 15 zuwa 16 na watan Yuni a birnin Lucerne na ƙasar Switzerland.

Za a wallafa sunayen ƙasashen da za su halarci wannan taro nan  gaba kaɗan, sai dai abin da ake da tabbaci a kai shine za a samu wakilci da kowace nahiya, da kuma kungiyoyin G7, G20  da BRICS.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.