Isa ga babban shafi

Gwamnan Kaduna ya mika daliban Kuriga ga iyayensu

Gwamnan jihar Kaduna da ke Najeriya, Sanata Uba Sani ya mika daliban makarantar Kuriga ga iyayensu bayan sun shafe kimanin sa'o'i 48 a hannun gwamnati ana kula da lafiyarsu sakamakon wahalar da suka sha a hannun 'yan bindigar da suka yi garkuwa da su.

Gwamnan Kaduna Uba Sani a yayin mika daliban makarantyar Kuriga ga iyayensu.
Gwamnan Kaduna Uba Sani a yayin mika daliban makarantyar Kuriga ga iyayensu. © Kaduna State Governor
Talla

Gwamnan ne ya sanar da mika daliban a shafinsa na Facebook a wannan Alhamis, yana mai cewa, ya mika daliban cikin sosuwar zuciya.

Gwamnan ya tabbatar cewa, sai da aka tabbatar da cikakkiyar lafiyar jiki da ta kwakwaluwar daliban kafin yanke shawarar mika su ga iyayensu da suka dade cikin zumudin haduwa da yaran nasu.

Uba Sani na yi wa daliban ban-kwana
Uba Sani na yi wa daliban ban-kwana © Kaduna State Governor

Gwamnan ya kara da cewa, daliban wadanda ya dauka a matsayin 'ya'yansa na ciki sun yi masa alkawarin cewa, za su mance da mummunar jarrabawar da ta same su tare da mayar da hankali kan karatunsu.

Domin nuna godiya kan jajircewar da yaran suka nuna, da kuma tsayin-dakarsu kan cimma burinsu na neman ilimi duk da mummunan ibtila'in da ya same su, gidauniyar Uba Sani za ta dauki nauyin karatunsu har zuwa matakin makarantar gaba da sakandare.

A bangare guda, gwamnan na Kaduna ya yi alkawarin cewa, zai biya diyya da iyalan Malam Abubakar wanda ya rasa ransa a hannun 'yan bindigar da suka kaddamar da farmaki kan makarantar ta Kuriga, inda gwamnan ya ce, zai bai wa iyalan nasa diyyar naira miliyan 10.

Wani bangare na daliban Kuriga a gidan gwamnatin jihar Kaduna.
Wani bangare na daliban Kuriga a gidan gwamnatin jihar Kaduna. © Kaduna State Governor

Sannan gwamnatin Kaduna za ta dauki nauyin karatun 'ya'yansa har zuwa matakin makarantar gaba da sakadanre kamar yadda sanarwar  ta shafin Facebook ta yi karin bayani.

Wani bangare na daliban Kuriga a gidan gwamnatin jihar Kaduna.
Wani bangare na daliban Kuriga a gidan gwamnatin jihar Kaduna. © Kaduna State Governor

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.