Isa ga babban shafi
France

Mutane 15 suka mutu a Faransa sanadiyyar ambaliya

Mamakon ruwan sama da aka kwarara kamar da bakin kwarya a kudancin kasar Faransa ya haddasa mummunar ambaliya da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 15, wasu da dama suka bace bat.Daruruwan mutane suka sami agajin jami’an kashe gobara, bayan da ruwan ya rutsa dasu a cikin gidaje da motoci da kuma kan rufin gine-gine.Dole sai da aka dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa daga Toulon zuwa Saint- Raphael, kuma jirage masu saukar angulu ne ke ceton rayukan mutane zuwa garin Draguignan, dake da yawan mutane dubu 40 in an doshi tsibirin kogin Meditareniya.  

Mazauna Draguignan na kauracewa- 16 juin 2010.
Mazauna Draguignan na kauracewa- 16 juin 2010. REUTERS/Sebastien Nogier
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.