Isa ga babban shafi
Faransa

Macron na ziyara a yankin da Faransa ta taba gwajin makamin Nukiliya

Shugaban Faransa Emmanuel Macron na fuskantar matsin lamba don neman gafara kan mummunan tasirin da gwajin nukiliya ya yi shekaru da dama dai-dai lokacin da ya fara ziyarar aiki ta farko zuwa yankin Polynesia da lamarin ya shafa.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin ziyara yankin Polynesia 24-07-21.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin ziyara yankin Polynesia 24-07-21. AFP - LUDOVIC MARIN
Talla

A ziyarar tasa ta kwanaki hudu, Macron zaiyi kokarin kwantar da hankulan al’ummar yankin kan batun na gwajin makamin nukiliya daga shekarar 1966 zuwa 1996, wato lokacin da Faransa ta kera makamin Nukiliya.

Macron zai kuma tattauna muhimmiyar batutuwa da suka hada rawar da yankin dake kudu maso gabashin tekun Pacific ke da shi, da kuma batun dumamar yanayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.