Faransa za ta ci gaba da matsin lambar tsagaita bude wuta a Gaza
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana kudurin kasar sa na sanya matsin lambar ganin Isra'ila ta tsagaita ruwan bama-bamai a yankin zirin Gaza.
Wallafawa ranar:
Kasashen Rasha da China sun yi watsi da daftarin kudirin da Amurka ta gabatar a hedkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sha alwashin ci gaba da matsa lamba kan shirin tsagaita wuta a zirin Gaza a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, bayan da kasashen China da Rasha suka ki amincewa da daftarin kudurin da Amurka ke marawa baya.
Sai dai Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya dage zamansa kan batun tsagaita wuta a Gaza zuwa ranar litinin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu