Isa ga babban shafi

Turkiyya da Italiya na neman maye gurbin Faransa a Afirika

Turkiyya da Italiya sun bayyana fara samun matsaya guda a kokarin da suke yi na fadada tasirinsu na tattalin arziki da diflomasiyya a nahiyar Afirka.

Firaministar Italiya Giorgia Meloni (daga hagu) zaune tare da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan (daga dama) yayin taron G20 a ranar 15 ga watan Nuwambar 2022 a birnin Nusa Dua na kasar Indonesia.
Firaministar Italiya Giorgia Meloni (daga hagu) zaune tare da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan (daga dama) yayin taron G20 a ranar 15 ga watan Nuwambar 2022 a birnin Nusa Dua na kasar Indonesia. © Leon Neal/Pool via REUTERS
Talla

Kasashen biyu, na neman damar yin hadin gwiwa da kasashen nahiyar a fannin tsaro, makamashi da kuma bakin haure, a daidai lokacin da daddadiyar tasirin Faransa a Africa ke raguwa.

A wannan watan ne majalisar dokokin Somaliya ta amince da wata yarjejeniya da Turkiyya na ba da kariya da taimakon ruwa a fannin gina sojojin ruwan Somaliya, wani mataki ne a yunkurin da Turkiyya ke yi na fadada ayyukanta a Afirka.

Yarjejeniyar ta tsaro ta biyo bayan yarjejeniyar da kasashen biyu suka cimma kan hakar makamashi a Somaliya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.